Tuni dai alamu ke nuna cewa an samu rarrabuwar kawuna a tsakanin 'yan majalisar, bisa dalilai na bambancin jam'iyyun siyasa da bangaranci.
Majalisar za ta jefa kuri'a kan batun idan bakin 'yan majalisar bai zo daya ba yayin muhawarar.
A makon jiya ne Majalisar Wakilan kasar ta amince da tsawaita dokar da watanni shida, a jihohin Borno da Yobe da kuma Adamawa.ABNA.